RFI Hausa सार्वजनिक
[search 0]
अधिक
Download the App!
show episodes
 
Artwork

1
Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

RFI Hausa

Unsubscribe
Unsubscribe
साप्ताहिक+
 
Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Al’umma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalin’ariziki, al’adu da dai sauransu…
  continue reading
 
Artwork

1
Wasanni

RFI Hausa

Unsubscribe
Unsubscribe
मासिक+
 
A kowace Litinin da Juma'a a shirye-shiryen Safe da Dare ana gabatar da Shirin Duniyar Wasanni akan batutuwa daban-daban da suka shafi wasanni a sassan duniya.
  continue reading
 
Artwork

1
Kasuwanci

RFI Hausa

Unsubscribe
Unsubscribe
मासिक+
 
Shirin yakan duba yadda kasuwanci da tattalin arizikin kasashen duniya ke ciki. Kana yakan ji sabbin dubaru da hanyoyin ci gaban tattalin arzikin na kasashen duniya. Tare da jin ta bakin 'Yan kasuwa da Masana’antu dangane da halin da suke ciki.
  continue reading
 
Artwork

1
Al'adun Gargajiya

RFI Hausa

Unsubscribe
Unsubscribe
मासिक+
 
Kawo al’adu na zamani da wadanda suka shude daga sassan kasashen duniya domin mai sauraro ya san cewa, duniyarmu tana da girma da yawan jama’a masu al’adu daban-dabam. Akwai kuma Shirin al'adunmu na musamman na karshen mako da mu ke gabatarwa a ranakun Asabar da lahadi.
  continue reading
 
Artwork

1
Mu Zagaya Duniya

RFI Hausa

Unsubscribe
Unsubscribe
साप्ताहिक
 
Shirin Mu Zagaya Duniya na duba Wasu Muhimman Labarai da suka ja hankalin Duniya a cikin mako. Ana gabatar da shirin ne a ranar Asabar da safe a kuma maimaita ranar Lahadi da daddare.
  continue reading
 
Artwork

1
Lafiya Jari ce

RFI Hausa

Unsubscribe
Unsubscribe
मासिक+
 
Shirin Lafiya Jari ce na tattaunawa da likitoci da mahukunta a game da kiyon lafiyar jama’a, sanin sabbin magunguna da binciken kimiya ya samar. Ana gabatar da shirin a ranar Littinin da hantsi, tare da maimaici a ranar Jumma'a da safe.
  continue reading
 
Artwork
 
Wannan Shirin ya shafi Fadakar da al'umma game da ci gaban da aka samu a sha'anin Ilimi a fannoni daban-daban na duniya, tare da nazari kan irin ci gaban da aka samu wajen binciken kimiya da fasaha da ke neman saukakawa Dan’adam wajen tafiyar da rayuwarsa a duniya. Shirin kuma zai yi kokarin jin irin bincike da masana ke yi domin inganta rayuwar Bil’adama. Shirin na zo maku ne, a duk ranar Talata a shirye-shiryenmu na safe, a ku maimata ranar Alhamis.
  continue reading
 
Artwork

1
Dandalin Siyasa

RFI Hausa

Unsubscribe
Unsubscribe
मासिक
 
Shirin Dandalin Siyasa, yana tattaunawa tare da tafka muhawar kan al’amurran siyasa da ke faruwa a kasashen duniya, da batutuwan da suka shafi al’umma kai tsaye, wanda Bashir Ibrahim Idris ke jagoranta. Wannan Shirin na zuwa ne a karshen mako Ranar Assabar da maimaci a ranar Lahadi a Shirye Shiryen Safe da Yamma.
  continue reading
 
Fili ne na musamman kan Fina-finai ta hanyar tattauna da masu ruwa da tsaki a wannan fanni a duniya, Tare da wayar wa ma su sauraro kai da kara masu basira dangane da hikimar da Allah ya bai wa wasu ta fanin shirya fim ko tsara wasan kwaikwayo. Wanda ke zo maku a duk ranar Asabar da safe, tare da maimaici a ranar Lahadi da yamma.
  continue reading
 
Shirin Al’adu, kida da fina-finai, shiri ne da ke zo maku a ranakun assabar da kafe 5:30 na yamma, tare da maimaici da karfe 8:00 na safiyar ranar Lahadi.Inda muke kawo ma ku rahotanni da labaran da suka shafi Fina-finai na gida da ketare, firarraki da mawakammu na gargajiya da na zamani, tare da kawo maku labaran da suka shafi al’adummu na gida da ketare. Tare da naku Mahaman Salisu Hamisu.
  continue reading
 
Loading …
show series
 
Ra'ayoyin masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali kan yadda aka kwashe watanni biyu bayan da shugaban kasa ya umarci hafsoshin tsaro da su tare a jihar Sokoto don tabbatar da tsaro, amma har yanzu 'yan bindiga na ci gaba da kai hare-hare ba kakkautawa. Shin ko me ke haifar da tarnaki ga kokarin tabbatar da tsaro a arewacin Najeriya? Danna a…
  continue reading
 
Shirin al'adunmu na gado tare da Aboulaye Issa, ya mayar da hankali ne kan al'adar gaɗa da ke ƙoƙarin gushewa tsakanin al'ummar Hausawa duk da tasirinta a shekarun baya musamman tsakanin matasa.द्वारा RFI Hausa
  continue reading
 
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon yayi duba ne kan ƙalubalen da fannin lafiya ke fuskanta na yadda ake gani a halin yanzu jama’a ke tsoro ko kuma kaucewa gwaje-gwajen lafiya ciki kuwa da har da wajibi da suka ƙunshi hawajini da nau’in jini ko kuma rukuninsa duk kuwa da muhimmancin hakan ga lafiyarsu. A baya-bayan nan bincike ya gano yadda jama’a…
  continue reading
 
Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci yayi duba ne kan danbarwar da aka samu tsakanin Najeriya da Libya. A makon daya gaba ne dai aka fara kai ruwa rana tsakanin bayan da tawagar Super Eagles ta Najeriya ta yi tattaki zuwa Libya don karawa da takwaransu ta ƙasar a wasa na biyu na neman gurbin zuwa gasar lashe kofin Afrika da za ayi a Morocco a she…
  continue reading
 
Shirin ‘Muhallinka Rayuwarka’ na wannan makon zai mayar da hankali ne a kan matsalar karancin nama da aka shiga a sassa da dama na Najeriya, inda za mu je jihar Adamawa a arewa maso gabashin kasar don jin yadda ake ciki da kuma inda matsalar ta ke.द्वारा RFI Hausa
  continue reading
 
Yayin da ‘Yan Najeriya da dama ke jin jiki kan matsin rayuwar da suka shiga tun bayan janye tallafin man fetur da kuma fara aiwatar da wasu matakai da sabuwar gwamnatin ƙasar ta yi, Bankin Duniya yayi gargaɗin cewar, matsalar da ake ciki samin taɓi ce, muddin aka kuskura aka janye ko dakatar da manufofin tattalin arziƙin da shugaba Tinubu ke aiwata…
  continue reading
 
Bankin Duniya, ya ce Najeriya da wasu ƙasashe da dama masu tasowa, za su iya shafe tsawon shekara ɗari a nan gaba kafin su yi nasarar rage kaifin talauci da ke addabar al’ummominsu. Wannan gargaɗi na Bankin Duniya na zuwa ne a daidai lokacin da bayanai ke cewa kusan a kowace rana ta Allah ana samun karuwar mutanen da suka dogara da malauna ne domin…
  continue reading
 
Shirin kasuwa a kai miki dole na wanna mako ya yi tattaki zuwa taron masu ruwa da tsaki ne a fannin bunkasa tattalin arziki ta kafofin internet wadda a turance ake kira digital economic wanda aka gabatar a jihar Lagos a tarayyar Najeriya.द्वारा RFI Hausa
  continue reading
 
Shirin ra'ayoyin masu sauraro na wannan rana ya maida hankali ne kan yadda tawagar kwallon Najeriya Super Eagles ta kaurace wa buga wasa da takwararta ta Libya sakamakon taskun da suka ci karo da shi lokacin isarsu a lasar ta Libya. Tuni gwamnatin Najeriya ta gayyaci jakadan Libya da ke Abuja don bayyana rashin amincewa da yadda aka tozartar da ƴan…
  continue reading
 
Shirin na wannan rana ya duba yadda wasu gwamnonin a Najeriya ke daukar alhakin tura yaran talakawa wasu kasashe domin karatu amma kuma daga bisani sai gwamnatin ta yi biris da sha'aninsu.द्वारा RFI Hausa
  continue reading
 
Gwamnantin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta sanar da ƙwace wa mutane 9 dukanninsu makusanta ga hamɓararren shugaban kasar Mohamed Bazoum shaidar zama ɗan ƙasa saboda zarginsu da shirya wa ƙasa zagon-ƙasa. Tsohon madugun ƴan tawaye Rissa Ag Boula da kuma Janar-Janar biyu na soji na daga cikin waɗanda wannan mataki ya shafa. Ku latsa alamar sauti dom…
  continue reading
 
Shirin a wannan makon ya maida hankali ke kan yadda aka faro gasar Firimiyar Ingila, inda akwa yanzu kowace ƙungiya ta samu nasarar buga wasanni 7-7. Tuni gasar ta soma nisa, inda Liverpool take a saman teburi da maki 18, yayinda Arsenal da Manchester City ke biye mata da maki, 17, kowannen su. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tar…
  continue reading
 
Shirin lafiya jari ce a wannan makon ya mayar da hankali ne game da matsalar shaye-shayen magunguna ba bisa ka'ida ko kuma shawarwarin masana kiwon kiwon lafiya ba, wadda hakan ke haifar da matsaloli da dama a jikin dan'adam. 14/10/2024द्वारा RFI Hausa
  continue reading
 
A yau Shirin zai mayar da hankali ne kan wani babban Taron karawa juna ilimi kan harkokin samar da abinci da bunkasa noma a Jihar Kano dake arewacin Najeriya Karkashin kulawar bankin Musulunci da Gidaunaiyar Bill and Melinda da Gidaunaiyar sarki Salman Wanda kungiyar harkokin noma ta SASAKAWA Africa ke jagoranta.…
  continue reading
 
Shirin Mu Zagaya duniya tare da Nura Ado Suleiman kamar ko yaushe ya yi bita ne kan muhimman labaran da suka faru a makon da muke bankwana da shi, ciki kuwa har da ƙarin farashin man fetur ta Najeriya ta sake yi karo na 4 cikin watanni 16 duk da matsi da tsadar rayuwa da ta addabi al'ummar ƙasar.द्वारा RFI Hausa
  continue reading
 
Najeriya ta yi sabon ƙarin farashin mai da akalla kashi 15%, wanda kuma shi ne karo na 4 a cikin watanni 16 da shugaba Bola Tinubu ya shafe kan karagar mulki. Babu dai wani dalili da kamfanin NNPCL da ke matsayin wakilin gwamnati a harkar mai ya bayar dangane da wannan farashi, illa kawai jama’a sun gan shi ne haka kwatsam. Kan wannan batu shirin '…
  continue reading
 
A Najeriya, yayin a ke fama da matsalar tattalin arziki da tsanantar harkokin rayuwa, alkaluma na tabbatar da cewa bankunan ƙasar na ci gaba samun gagarumar riba a kowace rana ta Allah. Shin ko meye dalilin wannan gibi tsakanin bankuna da kuma al’umma? Wane gyara ya kamata ayi domin tabbatar da cewa arzikin kasa na zagayawa a cikin al’umma? Wannan …
  continue reading
 
Shirin Kasuwa Akai Miki Dole na wannan makon ya maida hankali ne kan hada-hadar kasuwaci tsakanin Najeriya da makwabciyarta Kamaru, da irin kalubalen da ƴan kasuwar Kamaru da diribobi daga ƙasashen biyu ke fadi tashi a kan iyakokin ƙasashen biyu. Ƴan kasuwar ƙasashen biyu na amfana da juna, a wasu manyan hanyoyin 10 da a hukumance aka san da su da …
  continue reading
 
A Najeriya, yanzu haka wasu sun fara nuna fargaba a game da yadda tsarin dimokuradiyya ke gudana a kasar, musamman lura da yadda da zarar aka gudanar da zaben kananan hukumomi, to ko shakka babu jam’iyyar da ke rike da kujerar gwamna ce za ta lashe zaben babu tantama. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da aka bai wa kananan hukumomin damar cin …
  continue reading
 
Shirin Al'adu na wannan makon ya duba irin yanda masarautunmu na gargajiya ke kama hanyar zama ƙasa da ƙasa ta yanda sarakunan wasu masarautun ke nada ƴan wasu ƙasashe don basu mukamin a fadodinsu da sunan ƙarfafa zumunci da kyautata rayuwar jama'ar ƙasashen. A baya-bayan nan, mai Martaba Sarkin Damagaram da ke Jamhuriyar Nijar ya naɗa Alhaji Idris…
  continue reading
 
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan makon ya duba yadda wasu manyan jami’o’i a Najeriya ke neman tallafin ƙasashen da suka ci gaba kan yadda za a inganta ƙirƙirarriyar fasaha ta AI. Tuni kuma suka gabatar da wannan buƙata tasu a wajen taron da ƙungiyar bunkasa ilimi ta ƙasashen Turai kan shirya duk shekara, inda a wannan shekara Faransa ta karbi b…
  continue reading
 
Yau 7 ga watan oktoban shekarar daya kenan da mayakan Hamas suka kaddamar da hare-hare a Isra’ila, inda suka kashe mutane 1 da 200 tare da yin garkuwa da wasu akalla 150. Wannan ya fusata Isra’ila inda ta mayar da martani ta hanyar kashe sama da mutane kusan dubu 43 a yankin Gaza, tare da yaduwar wannan rikici zuwa kasashen Lebanan da Iran. Shin me…
  continue reading
 
Shirin lafiya jari ce a wannan makon ya mayar da hankali ne game da matsalar zuƙar taba sigari a cikin al'umma saɓanin wasu keɓantattun wurare da doka ta tanada. Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce a duk shekara sama da mutane miliyan 8 ne ke mutuwa sanadiyar shakar hayakin taba sigari kuma daga cikin wancan adadi, akwai sama da yara dubu 65 waɗanda…
  continue reading
 
Shirin Duniyar Wasanni na wannan lokaci yayi duba ne kan komen da Kyaftin din tawagar Najeriya Ahmed Musa ya yi wa tsohon ƙungiyarsa Kano Pillars tare da abokin wasansa Shehu Abdullahi. A karshen makon da muka yi bankwana da shi ne dai ƙungiyar kwallo ƙafa ta Kano Pillars a hukumance ta sanar da kulla yarjejeniyar shekara guda da ƴan wasan. Ku lats…
  continue reading
 
Shirin 'Muhallinka Rayuwarka na wannan makon ya tattauna ne akan yadda gwamnatin jihar Jigawa ta samar da cibiyoyin tafi da gidanka sama da 300, domin kula da lafiyar dabbobi. Mahukuntan na Jigawa sun kuma samar da wuraren sarrafa nama da kuma madara, matakan da suka sun ɗauka domin bunƙasa harkar kiwo da zummar mayar da shi na zamani.…
  continue reading
 
Daga cikin Labarun da suka fi ɗaukar hankali a makon da ya ƙare akwai jerin makamai masu linzamin da Iran ta kai wa Isra’ila hari da su, a yayin da ita kuma Isra’ilar ta karkatar da hare-haren da take kai wa a Gaza zuwa Kudancin Lebanon, h da zummar murkushe mayakan Hezbolla A Najeriya kuwa ɗimbin Iyallai ne suka shiga alhinin rashin da suka yi, bi…
  continue reading
 
Shirin Al’adun mu na Gado a wannan makon yayi duba ne kan yadda ake gudanar da bikin Sallar Gani. ita dai wannan sallar na daga cikin dadadun al’adar mallam Bahaushe, kuma har yanzu ana gudanar da wannan biki a wasu masarautu a Arewacin Najeriya da kuma Jamhuriyar Nijar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Abdoulaye Issa.....…
  continue reading
 
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan makon ya tattauna ne akan yadda makarantun manya ko kuma na yaƙi da jahilci kamar yadda akan kira su, ke fuskantar ƙalubalen ɗauka ko ilimantar da ɗaliban da yawansu ke ƙaruwa a kullum, adadin da ya zarta na makarantun manyan da ake da su. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Aisha Shehu Ka…
  continue reading
 
Shirin lafiya jari ce a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda ake ganin ƙaruwar masu fama da cutar amasonin jini, ko Sickler ko kuma Emasi, batun da ke da alaƙa ta kai tsaye da auratayyar da ake yi tsakanin masu nau’ikan jinin da masana ke gargaɗi kan illar da hakan ke da shi ga ƴaƴan da za su haifa. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken…
  continue reading
 
A dai-dai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiyen wasannin sharen fagen samun gurbi a gasar lashe kofin Afrika, Hukumar Kula Ƙwallon kafar Afrika CAF ta ce filayen wasan ƙasar Ghana ba su da ingancin da ya kamata a ce an gudanar da manyan wasanni na kasa da kasa a cikin, matakin da ke kara nuna gazawar ƙasar. Ita dai hukumar CAF ta ce ba komai ya s…
  continue reading
 
Shirin Muhallinka rayuwarka tare da Michael Kuduson ya mayar da hankali kan yadda wata al’ada da ake kira ''a ci ba'' dadi da ke zama babbar matsala ga manoma yayin girbin albarkar noma, a cikin wannan shiri za ku ji yadda manoman ke kokawa da yadda wannan al'ada ke kassara su, a wani yanayi da matsi baya ga tsadar kayakin noma ke ci gaba da ta'azz…
  continue reading
 
Daga cikin labarun da shirin Mu Zagaya Duniya na wannan makon ya waiwaya, akwai yadda babban taron zauren Majalisar Ɗinkin Duniya ya gudana, haka nan akwai bitar rahoton maƙudan ƙuɗaɗen da ECOWAS ta ware don samar da wutar lantarki a makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya, a wasu ƙasashen da ke ƙarƙashinta ciki har da Najeriya, haka nan shirin ya waiw…
  continue reading
 
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan makon tare da Ahmed Abba ya leka ne jihar Barno da ke arewa maso gabashin Najeriya, inda ya mayar da hankali kan tasarin tattalin arziki da ambaliyar baya-bayan nan ya haifarwa jihar da ma al'ummarta. Makonni biyu kenan tun bayan mummunar ambaliyar ruwa da ta afkawa wasu anguwannin birinin maiduguri na jiha…
  continue reading
 
Shirin namu na wannan mako zai yi dubi ne kan yadda hukumar kula da harkar jarabawan shiga jami’o’i a Najeriya wato JAMB da hadin guiwan kungiyar zabiya na kasa ta shirya taron nahiyar Afrika na farko kan baiwa nakasassu ko masu larura ta musamman dangane da harkar ilimi kamar kowani dan adam. Taron an shirya shi ne dai la’akari da irin kalubalen d…
  continue reading
 
A wannan makon shirin ya mayar da hankali ne kan abubuwan da ke haddasa cutar koda, la'akari da yadda cutar ke tsananta a wannan lokaci musamman a kasashe irin Najeriya, sabanin a lokutan baya da ba kasafai ake ganinta ba, baya ga karancin wuraren wankin kodar da ake fama dasu wato dialysis centers a turance. Wani bincike na baya-bayan nan na nuni …
  continue reading
 
Shirin a wannan lokaci zai leka gasar Firimirar Najeriya wato NPFL Wanda aka shiga mako na uku da somawa. Gasar Firimiyar Najeriya na daga cikin manyan gasannin Lik-lik da ake ji da su a nahiyar Afrika, musamman idan akayi la’akari da yadda ƙungiyoyin da ke fafatawa a wannan gasa ke taka rawar gani a gasar zakarun Ƙungiyoyin Afrika.…
  continue reading
 
Har yanzu tsuguni bata kare ba tsakanin kamfanin Dangote da kamfanin NNPC dangane da gabatar da man fetur da yake tacewa a cikin gida. A cikin wannan shirin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Kasum Kurfi, masanin tattalin arziki da kuma Abdulkarim Ibrahim dangane da kalubale da kuma mafita dangane da wannan al'amari.…
  continue reading
 
Shirin lafiya jarice na wannan mako ya mayar da hankali ne kan cutar katsewar laka wacce ke iya afkuwa a sanadiyar hadarin mota ko makamantansu da rikice-rikice ko fadowa daga wurare masu tudu da dai sauransu. Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirinद्वारा RFI Hausa
  continue reading
 
Loading …

त्वरित संदर्भ मार्गदर्शिका